Mutum 40 yan asalin karamar hukumar Faskari ta Jihar Katsina Sun Shaki Iskan yanci Sakamakon Salhu da akayi dasu.
Ɗan bindiga Isya Kwashen Garwa ya kara sako mutum 40 yan ƙaramar hukumar Faskari bayan an yi zaman sulhu da su
Ko a ranar Laraba yan bindigar sun saki mutum 30, in an haɗa da na yau sun sako mutum 70 daidai kenan
Sai dai Isya Kwashen Garwa ya nuna damuwar kan harin da ya zargi sojoji suka kai masu yau a Ruwangodiya daidai lokacin sallar Jumu'ah, inda ya ce muddin aka ci gaba da kashe masu yan uwa suma za su tada alƙawarin da akayi dasu agaban daruruwan al'umma.
Salwa radio and television online media services Katsina.
Category
Labarai